Isaiah 55:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَاشِ، ذَاكَ كِرَا أَلْعُمَّنْ دَ بَكَ سَنْسُبَ، أَلْعُمَّنْ دَ بَسُ سَنْكَبَ ذَاسُ غُدُ سُذُواْ وُرِنْكَ؞ ذَاسُيِ حَكَ غَمَا نِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكَ نٜىٰ، نِے مَيْ ڟَرْكِنَّنْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، نَاسَا أَغِرْمَمَكَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu kuwa za ku kira al'ummai, baƙi, Dā ba su kuwa san ku ba, ko da rana ɗaya, Amma yanzu za su sheƙo a guje domin su haɗa kai da ku! Ni, Ubangiji Allahnku, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Zan sa dukan wannan ya faru, Zan ba ku girma da daraja.”