Isaiah 56:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Su karnuka ne masu kwaɗayi; ba su taɓa ƙoshi. Su makiyaya ne marasa ganewa; duk sun nufi inda suka ga dama, kowa yana nemar wa kansa riba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُو كَرْنُكَ نٜىٰ مَاسُ ݣُوطَيِ، بَاسَ ڧُواْشِ؞ سُو مَاسُ كِيوُاْ نٜىٰ مَرَرْ غَانٜىٰوَ، كُواْوَنّٜىٰنْسُ يَجُويَ يَنَ بِنْ حَنْيَرْسَ، كُواْوَ يَنَ تَنٜىٰمَ وَكَنْسَ رِيبَ كَوَيْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suna kama da karnuka masu zarin ci, ba su taɓa samun abin da ya ishe su ba. Makiyayan nan kuma ba haziƙai ba ne, dukansu, kowa ya nufi inda ya ga dama. Kowa yana ta nemar wa kansa riba.