Isaiah 58:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُواْوَثٜىٰ رَانَ سُنَ تَنٜىٰمَنَ، سُنَيِنْ كَمَرْ سُنَ مَرْمَرِنْ سَنِنْ حَنْيَتَ، سُنَيِنْ كَمَرْ سُو جَمَعَثٜىٰ مَيْ عَيْكَتَ أَدَلْثِے، كَمَرْ سُو جَمَعَثٜىٰ وَدَّ تَكٜىٰبِنْ عُمَرْنَنْ اللَّهْ نْسُ؞ سُنَ ضُواْڧُواْ إِنْيِ مُسُ شَرِيعَرْ غَسْكِيَ، كَمَرْ سُنَ مَرْمَرِنْ اللَّهْ يَذُواْ كُسَدَسُو؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Duk da haka suna ta nemana kowace rana, suna murna su san al'amurana, sai ka ce su al'umma ce wadda take aikata adalci, wadda kuma ba ta rabu da dokokin Allahnta ba. Suna roƙona in yi musu shari'ar adalci, suna murna su zo kusa da Allah.”