Isaiah 58:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَاكُيِ كِرَا، نِے يَهْوٜىٰهْ ذَنْ أَمْسَ، ذَاكُيِ كُوكَنْ نٜىٰمَنْ تَيْمَكُواْ، ذَنْ كُوَثٜىٰ، ‹غَا نِنَنْ؞› عِدَنْ كُكَ دَيْنَ يِنْ دَنِّيَ، كُكَ بَرْ زَرْغِنْ جُونَ دَ يِنْ بَڧَرْ مَغَنَ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan za ku yi kira, ni kuwa zan amsa, za ku yi kuka, ni kuwa zan ce muku, ‘Ga ni.’ “Idan kuka kawar da karkiya daga cikinku, kuka daina nuna wa juna yatsa, da faɗar mugayen maganganu,