Isaiah 59:21 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan ’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ «أَغَرٜىٰنِ، وَنَّنْ نٜىٰ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَتَ دَسُو؞ رُوحُنَ وَنْدَ يَكٜىٰ تَرٜىٰدَكُو دَ مَغَنَاتَ وَدَّ نَسَا بَاكِنْكُ، بَذَاسُ رَبُ دَكُوبَ، كُواْ كُوَ سُرَبُ دَغَ بَاكِنْ ذُرِيَرْكُ، كُواْ جِيكُواْكِنْ ذُرِيَرْكُ دَغَ يَنْذُ حَرْ أَبَدَا؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Amma ni, wannan shi ne alkawarina da su, Ruhuna da yake tare da ku, da kalmomina da na sa a bakunanku, ba za su rabu da bakunanku ba, ko daga bakunan 'ya'yanku, ko na jikokinku, tun daga wannan lokaci har abada.”