Isaiah 6:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نَثٜىٰ، «كَيْتُواْنَ! تَاوَتَاڧَارٜىٰ! غَمَا كُواْوَثٜىٰ مَغَنَرْ بَاكِنَ ذُنُوبِثٜىٰ، إِنَ كُمَ ذَمَ تَرٜىٰدَ مُتَنٜىٰنْ دَ كُواْوَثٜىٰ مَغَنَرْ بَاكِنْسُ ذُنُوبِثٜىٰ؞ عَمَّا دُكْدَهَكَ، عِدَنُونَ سُنْ غَ سَرْكِے، سُنْ غَ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai na ce, “Sa zuciyata ya ƙare! Na shiga uku! Kowace maganar da ta fito bakina zunubi ce, ina zaune a tsakanin mutane waɗanda duk maganarsu zunubi ce, ba ta da tsarki. Amma yanzu da idona na ga Sarki, Ubangiji Mai Runduna!”