Isaiah 60:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُبُنْ دُبَّنْ رَاڧُمَ ذَاسُ رُڢٜىٰ ڧَسَرْكِے، ڧأَنَانً رَاڧُمَ دَغَ مَدْيَنَ دَ عٜىٰڢَ، دَ وَطَنْدَ سُكٜىٰ دَغَ شٜىٰبَ ذَاسُذُواْ؞ ذَاسُ كَٰوُاْ ظِينَارِيَ دَ كَايَنْ تُرَارٜىٰ، مُتَنٜىٰنْسُ ذَاسُيِ شٜىٰلَرْ لَابَرِ، لَابَرِ مَيْ دَاطِے عَكَنْ أَبِنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَيِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Babban ayarin raƙuma zai zo daga Madayana da Efa. Za su zo daga Sheba, su kawo zinariya da kayan ƙanshi. Mutane za su ba da labari mai daɗi a kan abin da Allah ya yi!