Isaiah 62:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَذَاعَ ڧَارَثٜىٰ دَكٜىٰ «يَسَشِّيَ» بَ، كُواْ عَثٜىٰ دَ ڧَسَرْكِے «مَثٜىٰنْ دَ مِجِنْتَ يَرَبُ دَ عِتَ» بَ؞ عَمَّا ذَاعَ ثٜىٰ دَكٜىٰ، «إِنَ جِنْ دَاطِنْتَ»، عَكُمَثٜىٰ دَ ڧَسَرْكِے «أَمَرْيَ»؞ غَمَا يَهْوٜىٰهْ يَنَ جِنْ دَاطِنْكِ، ذَيْ كُوَ عَوْرِ ڧَسَرْكِے تَذَمَ أَمَرْيَرْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ba za a ƙara ce da ke, “Yasasshiya” ba, Ko a ce da ƙasarki, “Mata wadda Mijinta ya Rabu da Ita.” Sabon sunanki yanzu shi ne, “Wadda Allah ya Yarda da Ita.” Ƙasarki kuwa za a ce da ita, “Ta yi Aure da Farin Ciki,” Domin Ubangiji ya ji daɗinki, Zai kuwa zama kamar miji ga ƙasarki.