Isaiah 64:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكَنْمُ كَمَرْ وَنْدَ يَڧَظَنْتُ، دُكَنْ أَيُّكَنْمُ نَأَدَلْثِے سُنْ ذَمَ كَمَرْ ڟُمَّ مَيْ ڧَظَنْتَا؞ مُنْ بُوشٜىٰ كَمَرْ بُوسَشّٜىٰنْ غَنْيٜىٰ، لَيْڢُواْڢِنْمُ سُنْ ذَمَ كَمَرْ إِسْكَ مَيْ ڧَرْڢِے وَدَّ تَݣُوشٜىٰمُ تَتَڢِے دَمُو؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Dukanmu muka cika da zunubi har ayyukanmu mafi kyau ƙazamai ne duka. Saboda zunubanmu, muka zama kamar busassun ganyaye waɗanda iska take faucewa ta tafi da su.