Isaiah 65:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ، «غَ وَطَنْدَ بَسُ تَمْبَيٜىٰنِبَ، نَبَيَّنَ كَيْنَ؞ وَطَنْدَ بَسُ نٜىٰمٜىٰنِبَ، نَسَاسُ سُكَ سَامٜىٰنِ؞ غَ أَلْعُمَّرْ دَ بَتَكِرَا غَ سُونَنَبَ، سَيْ نَثٜىٰ، ‹غَا نِے نَنْ، غَا نِے نَنْ!›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Na shirya in amsa addu'o'in mutanena, amma ba su yi addu'a ba. Na yi shiri domin su same ni, amma ba su ko yi ƙoƙarin nemana ba. Al'ummar ba ta yi addu'a a gare ni ba, ko da yake a koyaushe ina a shirye domin in amsa cewa, ‘Ga ni nan, zan taimake ku.’