Isaiah 66:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «كُجِ مَغَنَاتَ، كُو دَ كُكٜىٰ غِرْمَمَ مَغَنَاتَ! یَنْعُوَنْكُ وَطَنْدَ سُكَڧِيكُ سُكَ كُواْرٜىٰكُ سَبُواْدَ كُكَ غِرْمَمَ سُونَنَ؞ سُنَ ثٜىٰوَ ‹بَرِ أَطَوْكَكَ يَهْوٜىٰهْ ، دُواْمِنْ مُغَ ڢَضٍ ثِكِنْكُ،› عَمَّا سُونٜىٰ ذَاسُ شَا كُنْيَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ku kasa kunne ga abin da Ubangiji yake faɗa, ku da kuke tsoronsa gama ya ce, “Domin kuna da aminci gare ni, waɗansu daga 'yan'uwanku suka ƙi ku, har ba su da hulɗar kome da ku. Suna yi muku ba'a suna cewa, ‘Muna so mu ga kuna murna, saboda haka bari a ɗaukaka Ubangiji.’ Amma su za su sha kunya!