Isaiah 8:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar ’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَيْ يِوُوَ وَنِ ذَيْ غَيَ مُكُ كُنٜىٰمِ شَوَرَا دَغَ بُواْكَيٜىٰ دَ مَاسُ حَطَكَيْ دَ رُوحُواْحِنْ مَتَتُّو، وَطَنْدَ سُكٜىٰ مَغَنَ كَمَرْ دُواْدُواْ دَ یَرْ مُرْيَ كَمَرْ ڟُنْڟُ؞ سُنَ ثٜىٰوَ «أَيْ، يَا كَمَاتَ مُتَنٜىٰ سُنٜىٰمِ شَوَرَا دَغَ أَلُّواْلِنْسُ، سُنٜىٰمِ رَعَيِنْ مَتَتُّو غَمٜىٰدَ رَايَيُّ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutane za su riƙa ce muku ku nemi shawarar 'yan bori da masu sihiri waɗanda suke shaƙe muryar, har ba a jin abin da suke faɗa. Za su ce, “Ai, ma, ya kamata mutane su nemi shawara daga aljannu, su kuma nemi shawarar matattu saboda masu rai.”