Jeremiah 12:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَا أَبِنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَڢَطَا غَمٜىٰدَ مُوغَيٜىٰنْ مَڨُوبْتَنْ مُتَنٜىٰنْسَ، مُتَنٜىٰنْ دَ سُكَ تَٻَ غَادُوانْدَ يَبَا جَمَعَرْسَ إِسْرَٰٓءِيلَ سُغَادَا؞ «ذَنْ تُمْٻُكٜىٰسُ دَغَ ڧَسَرْسُ، ذَنْ كُمَ تُمْٻُكٜىٰ غِدَنْ يَهُودَ دَغَ ثِكِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mugayen maƙwabtan Isra'ila waɗanda suka taɓa gādon da ya ba jama'arsa Isra'ila su gada. “Saboda haka zan tumɓuke su daga cikin ƙasarsu. Zan kuma tumɓuke mutanen Yahuza daga cikinsu.