Jeremiah 14:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، غَ أَبِنْدَ نِے يَهْوٜىٰهْ نَكٜىٰ ڢَطِ غَمٜىٰدَ أَنَّبَاوَنْ دَسُكٜىٰيِنْ أَنَّبْثِنْ ڧَضْيَا دَ سُونَنَ، كُواْدَيَكٜىٰ بَنْعَيْكٜىٰسُبَ، سُو دَسُكٜىٰ ثٜىٰوَ بَذَاعَغَ تَكُواْبِنْ يَاڧِ كُواْ يُنْوَ عَڧَسَرْ نَنْبَ؞ تُواْ، تَوُرِنْ تَكُواْبِنْ يَاڧِ دَ يُنْوَ نٜىٰ ذَاعَ هَلَّكَرْ دَ وَطَنَّنْ أَنَّبَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka ga abin da ni Ubangiji na ce a kan annabawan da suke yin annabci da sunana, ko da yake ban aike su ba, waɗanda suke cewa, ‘Takobi da yunwa ba za su shigo ƙasan nan ba.’ Za a hallaka su da takobi da yunwa.