Jeremiah 14:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko ’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتَنٜىٰ كُوَ وَطَنْدَ أَنَّبَاوَا سُكٜىٰيِ مُسُ أَنَّبْثِنْ ڧَضْيَارْ نَنْ، ذَاعَ جٜىٰڢَرْ دَسُو وَجٜىٰ عَكَنْ تِيتُنَنْ عُرُوشَلِيمَ؞ ذَاعَكَكَّشٜىٰسُ تَوُرِنْ تَكُواْبِنْ يَاڧِ دَ يُنْوَ؞ بَابُ كُمَ وَنْدَ ذَيْبِنّٜىٰسُ دَسُو دَمَاتَنْسُ دَیَیَنْسُ مَظَا دَ مَاتَا؞ عِ، ذَنْ جُويَا مُغُنْتَارْسُ تَكُواْمَ عَكَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutanen da suka yi wa annabci, za a jefar da su waje a kan titunan Urushalima, a karkashe su da yunwa da takobi, ba wanda zai binne su, da su, da matansu, da 'ya'yansu mata da maza. Zan sa muguntarsu ta koma kansu.