Jeremiah 16:4 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَاسُ مُتُ دَغَ مُوغُوَرْ ثُوتَا؞ بَابُ كُمَ وَنْدَ ذَيْ يِكُوكَنْ مُتُوَرْسُ، كُواْ كُوَ يَبِنّٜىٰسُ؞ غَوَوَّكِنْسُ ذَاعَ تَتَّاكٜىٰسُ كَمَرْ كَاشِنْ دَبَّ أَ ڢُسْكَرْ ڧَسَا؞ ذَاسُ مُتُ تَوُرِنْ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ، غَوَوَّكِنْسُ كُمَ ذَاسُ ذَمَ عَبِنْثِنْ ڟُنْڟَيٜىٰنْ سَرَرِنْ سَمَ دَ نَمُواْمِنْ دَاجِ عَڧَسَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi makoki dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba. Za su zama juji. Takobi da yunwa za su kashe su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.”