Jeremiah 16:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ «كَدَ كَشِغَ غِدَنْ دَ عَكٜىٰيِنْ كُوكَنْ مُتُوَ، كُواْ كَتَڢِے عِنْدَ عَكٜىٰيِنْ بَڧِنْ ثِكِ؞ غَمَا نَارِغَا نَا جَنْيٜىٰ سَلَمَتَ دَ ڧَوْنَتَ مَرَرْ ثَنْجَاوَا دَ جِنْڧَيْنَ دَغَ جَمَعَرْ نَنْ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuma ya ce, “Kada ka shiga gidan da ake makoki, ko ka tafi inda ake baƙin ciki, kada ka yi baƙin ciki saboda su, gama na ɗauke salamata, da ƙaunata, da jinƙaina daga wurin jama'an nan.