Jeremiah 16:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا نِے يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ، اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ نَثٜىٰ، غَاشِ ذَنْسَا مُرْيَرْ مُرْنَ دَ تَڢَضٍ ثِكِ دَ مُرْيَرْ أَنْ‌غُواْ دَ تَأَمَرْيَ سُٻَثٜىٰ دَغَ وُرِنَّنْ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ ذَنْيِ وَنَّنْ كُوَ أَعِدُوانْكُ دَ كُمَ أَ زَامَانِنْكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, zan sa muryar murna, da ta farin ciki, da ta ango, da ta amarya, su ƙare a wurin nan a idonka da zamaninka.