Jeremiah 17:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ مِنِ «تَڢِے كَڟَيَ عَبَاكِنْ ڧُواْڢَرْ جَمَعَ، عِنْدَ سَرَاكُنَنْ يَهُودَ سُكَنْ شِغُواْ سُڢِتَ؞ سَعَنً كَبِے تَسَوْرَنْ ڧُواْڢُواْڢِنْ عُرُوشَلِيمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Biliyaminu, wadda sarakunan Yahuza suke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukan ƙofofin Urushalima.