Jeremiah 17:26 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً مُتَنٜىٰ ذَاسُذُواْ دَغَ غَرُضُوً يَهُودَ دَ وُرَارٜىٰنْ دَسُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَ عُرُوشَلِيمَ؞ ذَاسُ ذُواْ دَغَ يَنْكِنْ بِلِيَامِنُ دَغَ يَنْكِنْ ڧأَنَانً تُدَّنْ يَهُودَ دَغَ يَنْكِنْ تُدَّيْ دَ كُمَ دَغَ نٜىٰغٜىٰبْ؞ دُكَنْسُ ذَاسُكَٰوُاْ هَدَايُنْ ڧُواْنَاوَا دَ وَطَنْسُ هَدَايُ دَ هَدَايُنْ حَڟِ دَ نَتُرَارٜىٰ دَ كُمَ ݣَوْتَيْ نَنُونَ غُواْدِيَ أَ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutane za su zo daga biranen Yahuza da wuraren da yake kewaye da Urushalima, daga ƙasar Biliyaminu, da ta Shefela, da ta ƙasar tuddai, da kuma ta Negeb, suna kawo hadayu na ƙonawa da sadakoki, da hadayu na sha, da na turare, za su kuma kawo hadayu na godiya a Haikalin Ubangiji.