Jeremiah 17:27 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹عَمَّا عِدَنْ بَكُيِ حَكَبَ، بَكُ كُمَ كَسَ كُنّٜىٰ غَرٜىٰنِبَ، بَكُ كُوَ كِيَايٜىٰ رَانَرْ هُوتُ تَمَكُواْ دَ ڟَرْكِے بَ، كُنْ كُمَ طَوْكِ كَايَ كُنْ شِغَ تَڧُواْڢُواْڢِنْ عُرُوشَلِيمَ أَ رَانَرْ هُوتُ تَمَكُواْ، تُواْ، ذَنْ كُنَّ وَ ڧُواْڢُواْڢِنْ عُرُوشَلِيمَ وُتَا؞ ذَاتَثِنْيٜىٰ غِدَاجٜىٰنْ سَرَاكُنَنْ عُرُوشَلِيمَ، بَ كُوَ ذَاعَ عِيَ عَكَشٜىٰتَبَ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma idan ba ku kasa kunne gare ni ba, ba ku kuwa kiyaye ranar Asabar da tsarki ba, kun kuma ɗauki kaya kun shiga ta ƙofofin Urushalima a ranar Asabar, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wuta. Za ta kuwa cinye fādodin Urushalima, ba kuwa za ta kasu ba.’ ”