Jeremiah 19:3 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya sarakunan Yahuda da kuma mutanen Urushalima. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku saurara! Zan kawo masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَڢَطَا وَسَرَاكُنَنْ يَهُودَ دَ مَذَوْنَنْ عُرُوشَلِيمَ مَغَنَاتَ ثٜىٰوَ ‹غَاشِ، نِے يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَنْ كَٰوُاْ وَتَ مَسِيڢَ أَوَنَّنْ وُرِے، إِرِنْ مَسِيڢَرْ دَ ذَاتَسَا دُكْ وَنْدَ يَجِ لَابَرِنْتَ ذَيْڢِرْغِتَ سُواْسَيْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya ku sarakunan Yahuza da mazaunan Urushalima, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, zan kawo wata irin masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa.