Jeremiah 19:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘A wannan wuri zan lalace dabarun Yahuda da na Urushalima. Zan sa a kashe su da takobi a gaban abokan gābansu, a hannuwan waɗanda suke neman ransu, zan kuma ba da gawawwakinsu su zama abinci ga tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ مَيْدَ شِرِنْ يَهُودَ دَ عُرُوشَلِيمَ أَبِنْ بَنْظَ أَوُرِنَّنْ؞ ذَنْسَا أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ سُكَكَّشٜىٰسُ دَ تَكُواْبِے، عِ، ذَنْسَا سُڢَاطَ أَ حَنُّنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ نٜىٰمَنْ رَنْسُ سُكَشٜىٰ؞ ذَنْ بَادَ غَوَوَّكِنْسُ سُذَمَ عَبِنْثِنْ ڟُنْڟَيٜىٰنْ سَرَرِنْ سَمَ دَ نَنَمُواْمِنْ دَاجِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A wannan wuri zan wofinta dabarun Yahuza da na Urushalima, zan sa a kashe jama'arsu da takobi, a gaban abokan gābansu, ta hannun waɗanda suke neman ransu. Zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.