Jeremiah 2:26 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«كَمَرْ يَدَّ ٻَرَوُاْ يَكَنْ شَا كُنْيَا سَعَدَّ عَكَ كَامَ شِ، حَكَنٜىٰ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَاسُشَا كُنْيَا، دَ سُو دَ سَرَاكُنَنْسُ دَ شُوغَبَنِّنْسُ، دَ ڢِرِسْتُواْثِنْسُ دَ أَنَّبَاوَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Kamar yadda ɓarawo yakan sha kunya sa'ad da aka kama shi, Haka nan mutanen Isra'ila za su sha kunya, Da su, da sarakunansu, da shugabanninsu, Da firistocinsu, da annabawansu.