Jeremiah 21:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَايَنْ وَنَّنْ، ذَنْ طَوْكِ سَرْكِے صَدِڧِيَ نَ يَهُودَ دَ دَتَّاوَنْسَ دَ مُتَنٜىٰنْسَ، وَطَنْدَ سُكَ كُٻُتَ دَغَ بَلَعِنْ دَ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ، إِنْ بَادَسُو أَ حَنُّنْ سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ دَ كُمَ أَ حَنُّنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ وَطَنْدَ سُكٜىٰ نٜىٰمَنْ رَايُكَنْسُ؞ سَرْكِنْ ذَيْ كَشٜىٰسُ دَ تَكُواْبِے؞ بَذَيْ بَرْسُبَ، بَذَيْ كُوَجِ تَوْسَيِنْسُ كُواْ يَيِ مُسُ جِنْڧَيْبَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Bayan wannan zan ceci Zadakiya Sarkin Yahuza, shi da bayinsa, da mutanen birnin nan waɗanda suka tsira daga annoba, da takobi, da yunwa, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, da hannun abokan gābansu, da waɗanda suke neman rayukansu. Zai kashe su da takobi, ba zai ji tausayinsu, ko ya rage waɗansunsu, ko ya ji juyayinsu ba.’