Jeremiah 21:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكْ وَنْدَ يَذَوْنَ عَثِكِنْ بِرْنِنَّنْ، ذَيْ مُتُ تَوُرِنْ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ دَ بَلَعِ؞ عَمَّا دُكْ وَنْدَ يَڢِتَ يَبَادَ كَنْسَ غَ كَلْدِيَاوَنْ دَ سُكَ كٜىٰوَيٜىٰكُ دَ يَاڧِ، ذَيْ رَايُ يَڟِيرَا دَ رَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Shi wanda ya zauna a birnin nan zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma shi wanda ya fita ya ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suke kewaye da ku zai rayu ya tserar da ransa.