Jeremiah 22:3 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹يِ غَسْكِيَ دَ أَدَلْثِے، كُكُٻُتَرْ دَ وَنْدَ عَكَيِ مَسَ ڨُوثٜىٰ دَغَ كُمَ حَنُّنْ مَاسُ يِمَسَ دَنِّيَ؞ كَدَ كُوُلَڧَنْتَ بَڧُواْ، كُواْ كُثُوثٜىٰشِ، كُواْ مَرَايُ، كُواْ مَاتَرْ دَ مِجِنْتَ يَمُتُ؞ كَدَ كُمَ كُظُبْدَ جِنِنْ مَرَسَ لَيْڢِے أَوَنَّنْ وُرِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka Ubangiji ya ce, ka yi gaskiya da adalci, ka ceci wanda ake masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka cuci baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, kada kuma ka zubar da jinin marasa laifi a wannan wuri.