Jeremiah 26:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan firistoci da annabawa suka ce wa fadawan da dukan mutane, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa gama ya yi annabci gāba da wannan birni. Ku kun ji da kunnuwanku!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ ڢِرِسْتُواْثِے دَ أَنَّبَاوَنَّنْ سُكَ ڢَطَا وَدَتَّاوَا دَ دُكَنْ جَمَعَ سُكَثٜىٰ «مُتُمِنَّنْ إِرْمِيَ يَثَنْثَنْثِ حُكُنْثِنْ مُتُوَ، غَمَا يَيِ أَنَّبْثِ نَغَابَادَ بِرْنِنَّنْ، يَدَّ كُكَجِ دَ كُنُّوَنْكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai firistoci da annabawa suka faɗa wa sarakunan nan da jama'a duka, suka ce, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa, gama ya yi annabci gāba da wannan birni kamar yadda kuka ji da kunnuwanku.”