Jeremiah 26:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ku tabbata dai, cewa in kuka kashe ni, za ku jawo wa kanku alhakin jini marar laifi a kanku da a kan birnin nan da kuma a kan masu zama a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا كُسَنِ ڢَا، بَابُ شَكَّ عِدَنْ كُكَ كَشٜىٰنِ، ذَاكُ جَٰوُاْ وَكَنْكُ أَلْحَكِنْ جِنِنْ مَرَرْ لَيْڢِے دَ كُمَ عَكَنْ بِرْنِنَّنْ دَ مَذَوْنَنْسَ؞ غَمَا غَسْكِيَرْ عِتَثٜىٰ يَهْوٜىٰهْ يَا عَيْكٜىٰنِ وُرِنْكُ دُواْمِنْ إِنْ ڢَطِ دُكَنْ مَغَنَرْ نَنْ عَكُنّٜىٰنْكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ku tabbata dai, idan kuka kashe ni, za ku jawo hakkin jinin marar laifi a kanku da a kan wannan birni da mazauna a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.”