Jeremiah 26:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Hezekiya sarkin Yahuda ko kuwa wani a Yahuda ya kashe shi? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji ya nemi tagomashinsa ba? Ubangiji kuwa bai yi juyayi ya kuma janye masifar da ya furta zai kawo a kansu ba? Muna gab da jawo wa kanmu muguwar masifa!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سُكَ ثِيغَبَدَ مَغَنَ ثٜىٰوَ «تُواْ، سَرْكِے هٜىٰزٜىٰكِيَ نَ يَهُودَ دَ دُكَنْ جَمَعَرْ يَهُودَ سُنْ كَشٜىٰ أَنَّبِے مِيكَ نٜىٰ؟ كُواْ كَطَنْ! بَ هٜىٰزٜىٰكِيَ يَجِڟُواْرُوانْ يَهْوٜىٰهْ ، يَضُواْڧِ يَهْوٜىٰهْ يَثَنْجَ نِيَّرْسَ غَمٜىٰدَ مَسِيڢَرْدَ يَشِرْيَ ذَيْ كَٰوُاْ عَكَنْسُ بَ؟ يَنْذُ مُنَ غَبْ دَ جَٰوُاْ وَكَنْمُ بَبَّرْ مَسِيڢَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ashe, Hezekiya Sarkin Yahuza da dukan Yahuza sun kashe shi ne? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji, ya roƙi alherinsa ba? Ashe, Ubangiji bai janye masifar da ya hurta a kansu ba? Yanzu fa gab muke da mu jawo wa kanmu babbar masifa.”