Jeremiah 27:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘ “Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹عَمَّا عِدَنْ وَتَ أَلْعُمَّ كُواْ وَنِ مُلْكِ يَڧِ يَبَوْتَاوَ سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ، كُواْ يَڧِ يَمِيڧَ وُيَنْسَ عَڧَرْڧَشِنْ إِيكُوانْ سَرْكِنْ كَمَرْ يَدَّ سَانِيَرْ نُواْمَ تَكَنْ مِيڧَ وُيَ ڧَرْڧَشِنْ غُنْغُمٜىٰ، ذَنْ حُكُنْتَ أَلْعُمَّرْ نَنْ دَ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ دَ بَلَعِ، حَرْ سَيْ نَهَلَّكَ أَلْعُمَّرْ نَنْ تَهَنُّنْ نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“ ‘Amma idan wata al'umma ko wani mulki bai yarda ya bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila ba, bai kuma ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyansa ba, zan hukunta wa wannan al'umma da takobi, da yunwa, da annoba, har in hallaka ta, ta hannun Nebukadnezzar, ni Ubangiji na faɗa.