Jeremiah 28:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa zan sa karkiyar ƙarfe a wuyan dukan waɗannan al’ummai don in sa su bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon, za su kuwa bauta masa. Zan ma sa shi ya mallaki namun jeji.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَاشِ، نَسَا غُنْغُمٜىٰنْ ڧَرْڢٜىٰ أَوُيَنْ دُكَنْ وَطَنَّنْ أَلْعُمَّيْ دُواْمِنْ سُبَوْتَاوَ سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ؞ ذَاسُ كُوَ بَوْتَا مَسَ، غَمَا نَا بَادَسُو أَ حَنُّنْسَ، حَرْ مَا دَ نَمُواْمِنْ دَاجِ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ، اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na faɗa. Na sa wa wuyan dukan waɗannan al'ummai karkiya ta ƙarfe, don su bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila, za su kuwa bauta masa, gama na ba shi su, har da namomin jeji.’ ”