Jeremiah 29:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni, ’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُواْ، غَ أَبِنْدَ نِے يَهْوٜىٰهْ نَثٜىٰ غَمٜىٰدَ سَرْكِے دَغَ ذُرِيَرْ دَاوُدَ دَ كُمَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ دَسُكٜىٰ ذَمَ عَبِرْنِنَّنْ، وَتُواْ غَمٜىٰدَ یَنْعُوَنْكُ وَطَنْدَ بَسُبِيكُ ذُوَا بَوْتَبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ku ji abin da Ubangiji ya faɗa a kan sarkin da ya hau gadon sarautar Dawuda, da a kan dukan jama'ar da suke zaune a wannan birni, wato a kan danginku waɗanda ba a kwashe su zuwa zaman talala ba.