Jeremiah 29:31 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَعَيْكَ دَ سَڧُواْ ذُوَاغَ دُكَنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ ذَمَنْ بَوْتَا يَثٜىٰ، «غَا أَبِنْدَ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا غَمٜىٰدَ شٜىٰمَيَ مُتُمِنْ نٜىٰهٜىٰلَمْ؞ شٜىٰمَيَ يَيِ مُكُ أَنَّبْثِ، كُواْدَيَكٜىٰ بَنْعَيْكٜىٰشِيبَ، يَكُمَسَا كُكَ دُواْغَضَ غَ ڧَضْيَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ya aika wa dukan waɗanda suke zaman talala ya ce, “Haka Ubangiji ya ce a kan Shemaiya mutumin Nehelam, ‘Saboda Shemaiya ya yi muku annabci, alhali ni ban aike shi ba, ya sa ku dogara ga ƙarya,’