Jeremiah 29:32 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِنِ يَهْوٜىٰهْ ، سَبُواْدَ حَكَ، غَاشِ، ذَنْ حُكُنْتَ شٜىٰمَيَ مُتُمِنْ نٜىٰهٜىٰلَمْ دَ ذُرِيَرْسَ؞ بَابُ كُواْ طَيَ دَغَ ثِكِنْ ذُرِيَرْسَ وَنْدَ ذَاعَ بَرِ دَ رَيْ ثِكِنْ وَنَّنْ جَمَعَ، بَابُ كُمَ وَنِنْسُ دَ ذَيْ غَ أَلْحٜىٰرِنْ دَ ذَنْيِ وَجَمَعَتَ؞ غَمَا يَيِ مَغَنَرْ تَاوَيٜىٰ عَكَيْنَ، نِے يَهْوٜىٰهْ ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
saboda haka Ubangiji ya ce, ‘ga shi, zan hukunta Shemaiya, mutumin Nehelam, shi da zuriyarsa ba za a bar masa mai rai ko ɗaya a wannan jama'a ba, wanda zai ga irin alherin da zan yi wa jama'ata, gama ya kuta tayarwa ga Ubangiji,’ ” in ji Ubangiji.