Jeremiah 3:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «مَيْ يِوُوَ مُتُمْ ذَيْ سَكِ مَاتَرْسَ تَتَڢِے تَكُمَ ذَمَ مَاتَرْ وَنِ؞ إِنْ يَيِ حَكَ، مُتُمِنْ يَنَ عِيَ دَاوُاْ دَ عِتَ؟ أَشٜىٰ، يِنْ حَكَ بَذَيْ ڧَظَنْتَرْدَ ڧَسَرْ بَ؟ يَا كٜىٰ إِسْرَٰٓءِيلَ، كِنْيِ كَارُوَنْثِنْكِ دَ مَسُواْيَ دَيَوَ؞ يَنْذُ كُمَ كِنَ سُواْ كِدَاوُاْ وُرِينَ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Idan mutum ya saki matarsa, Ta kuwa rabu da shi, har ta auri wani, Ya iya ya komo da ita? Ashe, yin haka ba zai ƙazantar da ƙasar ba? Ya Isra'ila, kin yi karuwanci, Abokan sha'anin karuwancinki, suna da yawa. Za ki sāke komowa wurina? Ni, Ubangiji, na faɗa.