Jeremiah 30:18 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “ ‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«إِنْجِنِ يَهْوٜىٰهْ ، غَاشِ، ذَنْ مَيَرْوَ ذُرِيَرْ يَعْڧُوبَ دَ أَلْبَرْكُنْتَ، إِنْجِ تَوْسَيِنْ وُرَارٜىٰنْ ذَمَنْتَ؞ ذَاعَ سَاكٜىٰ غِنَا بِرْنِنْ أَوُرِنْسَ نَدَا، عَكُمَ كَڢَ غِدَنْ سَرْكِے أَ عِنْدَ يَكٜىٰ أَدَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan komar wa alfarwar Yakubu arzikinta, Zan kuma nuna wa wuraren zamansa jinƙai, Za a sāke gina birnin a kufansa, Fādar kuma za ta kasance a inda take a dā.