Jeremiah 31:34 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتُمْ بَذَيْسَاكٜىٰ كُواْيَوَ مَڨُوبْثِنْسَ، كُواْ يَكُواْيَاوَ طَنْعُوَنْسَ ثٜىٰوَ ‹كُسَنْ يَهْوٜىٰهْ › بَ، غَمَا دُكَنْسُ ذَاسُسَنِّ، دَغَ مَڢِے ڧَرَمِ ذُوَا مَڢِے غِرْمَ عَثِكِنْسُ؞ ذَنْ غَاڢَرْتَا مُسُ لَيْڢُواْڢِنْسُ، بَكُوَ ذَنْ سَاكٜىٰ تُنَاوَا دَ ذُنُبَنْسُبَ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa, ko ɗan'uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji’ ba, gama su duka za su san ni, tun daga ƙarami har zuwa babba. Zan gafarta musu laifofinsu, ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.”