Jeremiah 32:24 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَاشِ، أَنْرِغَا أَنْتَارَ ڧَسَا دُواْمِنْ أَ هَوْ تَكَتَنْغَرْ بِرْنِنْ دُواْمِنْ يَاڧِ؞ تَوُرِنْ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ دَ بَلَعِ أَنْبَادَ بِرْنِنْ عُرُوشَلِيمَ أَ حَنُّنْ كَلْدِيَاوَا وَطَنْدَ سُكٜىٰ يَاڧِ دَ عِتَ يَنْذُ؞ أَبِنْدَ كَڢَطَا يَڢَرُ، كَيْ مَا دَ كَنْكَ كَغَنِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ga shi, Kaldiyawa sun gina mahaurai kewaye da birnin da suka kewaye shi da yaƙi. Saboda takobi, da yunwa, da annoba aka ba da birnin a hannun Kaldiyawa, waɗanda suke yaƙi da birnin. Abin da ka faɗa ya tabbata, ka kuwa gani.