Jeremiah 32:29 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَلْدِيَاوَنْ دَسُكٜىٰ يَاڧِ دَ بِرْنِنَّنْ ذَاسُذُواْ سُسَا مَسَ وُتَا سُڧُواْنٜىٰشِ، تَرٜىٰدَ دُكَنْ غِدَاجٜىٰ أَ عِنْدَ سُكَيِ أَبِنْدَ يَسَا نَيِ ڢُشِے، وَتُواْ وَطَنْدَ عَكَنْ رُڢِنْسُ نٜىٰ عَكٜىٰ ڧُواْنَ وَ بَعَلْ هَدَايُنْ تُرَارٜىٰ، عَكٜىٰ كُمَ مِيڧَ هَدَايُ نَشَا غَ وَطَنْسُ أَلُّواْلِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kaldiyawa da suke yaƙi da wannan birni za su zo, za su ƙone wannan birni da wuta ƙurmus, da gidaje waɗanda aka ƙona turare ga Ba'al a kan rufinsu. Aka kuma miƙa hadayu na sha ga gumaka, don su tsokane ni in yi fushi.