Jeremiah 32:44 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَوَنَّنْ ڧَسَا، ذَاعَ سَاكٜىٰ سَيٜىٰنْ ڢِيلَيٜىٰنْ غُواْنَ دَ كُطِ، أَسَا حَنُّ عَكَنْ تَكَرْدُنْ شَيْدَرْ سَيَ، أَ مَنَّا مُسُ هَاتِمِ أَغَبَنْ شَيْدُ عَيَنْكِنْ ڧَسَرْ بِلِيَامِنُ دَ وُرَارٜىٰنْ دَسُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَ عُرُوشَلِيمَ دَ ثِكِنْ غَرُضُوً يَهُودَ دَ غَرُضُوً يَنْكِنْ تُدَّيْ دَ غَرُضُوً دَسُكٜىٰ عَڧأَنَانً تُدَّيْ دَ غَرُضُوً دَسُكٜىٰ أَ نٜىٰغٜىٰبْ؞ غَمَا ذَنْ مَيَرْ مُسُ دَ أَلْبَرْكُنْسُ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za a sayi gonaki da kuɗi, a sa hannu a kan sharuɗa, a hatimce su a gaban shaidu, a ƙasar Biliyaminu da wuraren da suke kewaye da Urushalima, da cikin garuruwan Yahuza, da na garuruwan ƙasar tudu, da a garuruwan kwaruruka, da a garuruwan Negeb, gama zan komar wa mutane da wadatarsu a ƙasarsu, ni Ubangiji na faɗa.”