Jeremiah 36:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دُكَنْ دَتَّاوَنْ سُكَ عَيْكَ يٜىٰهُودِ طَنْ نٜىٰتَنِيَ، جِيكَنْ شٜىٰلٜىٰمِيَ طَنْ كُشِ، ذُوَا وُرِنْ بَرُكْ دَ ثٜىٰوَ «طَوْكِ لِتَّڢِنْدَ كَكَرَنْتَ عَكُنّٜىٰنْ مُتَنٜىٰ، كَذُواْ؞» سَيْ بَرُكْ طَنْ نٜىٰرِيَ يَطَوْكِ لِتَّڢِنْ أَ حَنُّنْسَ يَتَڢِے وُرِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai dukan sarakunan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya faɗa wa Baruk ya kawo littafin nan da ya karanta wa jama'a. Sai Baruk ɗan Neriya ya ɗauki littafin ya je wurinsu.