Jeremiah 36:29 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَيْثٜىٰ غَمٜىٰدَ سَرْكِے يٜىٰهُواْيَكِمْ «إِنْجِنِ يَهْوٜىٰهْ ، كَيْ كَا ڧُواْنٜىٰ نَطَطّٜىٰنْ لِتَّڢِ كَنَ ثٜىٰوَ ‹دُوانْمٜىٰ كَرُبُوتَ ثٜىٰوَ بَا شَكَّ سَرْكِنْ بَابِيلَ ذَيْذُواْ يَرُشٜىٰ ڧَسَرْ نَنْ، يَكَكَّشٜىٰ مُتَنٜىٰنْتَ دَ دَبُّواْبِنْتَ؟›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zai kuma ce wa Yehoyakim Sarkin Yahuza, “Haka Ubangiji ya ce maka, ka ƙone littafin, kana cewa, ‘Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle Sarkin Babila zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?’