Jeremiah 37:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے صَدِڧِيَ يَعَيْكَ عَكَٰوُاْ مَسَ إِرْمِيَ؞ سَرْكِے كُوَ يَتَمْبَيٜىٰشِ عَٻُواْيٜىٰ عَثِكِنْ غِدَنْسَ يَثٜىٰ «كُواْ أَݣَويْ مَغَنَ دَغَ وُرِنْ يَهْوٜىٰهْ ؟» سَيْ إِرْمِيَ يَأَمْسَ «عِ، أَݣَويْ!» يَثِيغَبَدَ مَغَنَ يَثٜىٰ «ذَاعَ بَادَكَيْ أَ حَنُّنْ سَرْكِنْ بَابِيلَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarki Zadakiya ya aika a kawo masa Irmiya. Sarki kuwa ya shigar da shi gidansa, ya tambaye shi a asirce, ya ce, “Ko akwai wata magana daga wurin Ubangiji?” Sai Irmiya ya ce, “Akwai kuwa!” Ya ci gaba ya ce, “Za a ba da kai a hannun Sarkin Babila.”