Jeremiah 37:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَڢَطَا وَ يٜىٰهُكَلْ دَ زَڢَنِيَ وَطَنْدَ سَرْكِے صَدِڧِيَ نَ يَهُودَ يَعَيْكٜىٰسُ سُيِ وَ يَهْوٜىٰهْ تَمْبَيَ، يَثٜىٰ «إِنْجِنِ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، كُواْدَيَكٜىٰ سُواْجُواْجِنْ سَرْكِے ڢِرْعَوْنَ نَ مَصَرْ سُنْذُواْ سُتَيْمَكٜىٰكُ، ذَاسُ كُواْمَ ڧَسَرْسُ مَصَرْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na ce ka faɗa wa Sarkin Yahuza wanda ya aiko ka ka tambaye ni, ka faɗa masa cewa, ‘Rundunar sojojin Fir'auna, wadda ta kawo maka gudunmawa tana gab da juyawa zuwa ƙasarta a Masar.