Jeremiah 38:4 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دَتَّاوَنْ سُكَثٜىٰ وَسَرْكِے «رَنْكَيَدَطٜىٰ! يَا كَمَاتَ عَكَشٜىٰ مُتُمِنَّنْ إِرْمِيَ غَمَا إِرِنْ مَغَنَرْسَ نَنْ يَنَ سَا سُواْجُواْجِنْ دَ سُكَ ضَغٜىٰ عَبِرْنِنْ سُڢِدَّ ذُوثِيَا، حَرْ مَا دَ دُكَنْ سَوْرَنْ جَمَعَ؞ غَمَا مُتُمِنَّنْ بَايَ نٜىٰمَنْ لَاڢِيَرْ جَمَعَرْ نَنْ، سَيْدَيْ وَهَلَ يَكٜىٰ نٜىٰمَ تَڢَاطُواْ مُسُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sarakunan suka ce wa sarki, “A kashe mutumin nan, gama yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran jama'a duka ta wurin irin maganganun da yake faɗa musu. Gama wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan jama'a sai dai wahala yake nemar musu.”