Jeremiah 40:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya sake shi a Rama. Ya sami Irmiya a daure da sarƙoƙi a cikin sauran kamammu daga Urushalima da kuma Yahuda waɗanda ake kaiwa zaman bauta a Babilon.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَا يِمَغَنَ دَ إِرْمِيَ بَايَنْدَ نٜىٰبُظَرَدَنْ شُوغَبَنْ یَنْ غَادِنْ سَرْكِے يَسَكِ إِرْمِيَ أَ رَمَ؞ دَا مَا نٜىٰبُظَرَدَنْ يَكَيْ إِرْمِيَ أَوُرِنْ أَطَوْرٜىٰ دَ سَرْڧَ، تَرٜىٰدَ مُتَنٜىٰنْ عُرُوشَلِيمَ دَ يَهُودَ وَطَنْدَ ذَاعَ كَيْسُ بَوْتَا عَ بَابِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya yi magana da Irmiya bayan da Nebuzaradan shugaban matsara ya sake shi daga Rama, sa'ad da ya yi masa ƙuƙumi tare da waɗanda aka kwaso daga Urushalima da Yahuza, za su Babila.