Jeremiah 43:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
« ‹سَعَدَّ يَذُواْ ذَنْسَا يَڧُواْنٜىٰ غِدَاجٜىٰنْ غُمَكَنْ ڧَسَرْ مَصَرْ، ذَيْ ڧُواْنٜىٰ وَطَنْسُ غُمَكَنْسُ يَݣُوشٜىٰ وَطَنْسُ ذُوَا ڧَسَرْسَ؞ ذَيْ كُمَ ڟَبْتَثٜىٰ دُكَنْ ڧَسَرْ مَصَرْ كَمَرْ يَدَّ مَكِيَايِ يَكَنْ كَكَّٻٜىٰ ݣُورْݣُوتَ دَغَ رِيغُنَنْسَ، ذَيْ كُوَ تَاشِ يَتَڢِے غِدَا لَاڢِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zai cinna wa gidajen gumakan Masar wuta, zai ƙone su, ya tafi da waɗansu, zai tsabtace ƙasar Masar kamar yadda makiyayi yakan kakkaɓe ƙwarƙwata daga cikin tufafinsa, zai kuwa tashi daga wurin lafiya.