Jeremiah 44:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ كَوَرْدَ ضَغُواْوَرْ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ، سُو دَ سُكَسَاكَيْ غَ ذَمَ عَڧَسَرْ مَصَرْ، ذَاسُ كُوَ هَلَّكَ أَ مَصَرْ؞ دَغَ ڧَرَمِ ذُوَا بَبَّ ذَاسُ مُتُ تَوُرِنْ تَكُواْبِے دَ يُنْوَ؞ ذَاسُ ذَمَ كَمَرْ أَبِنْ بَنْظَ دَ أَبِنْ ڟُواْرُواْ دَ أَبِنْ لَعَنَ دَ أَبِنْ ذَاغِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sauran mutanen Yahuza kuwa waɗanda suka ragu, waɗanda suke niyyar zuwa ƙasar Masar da zama, zan sa dukansu su halaka a can. Takobi da yunwa za su kashe dukansu a Masar, da yaro da babba. Za su zama abin la'antawa, da abin tausayi, da abin zargi, da abin kunya.