Jeremiah 44:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«عَمَّا كُجِ أَبِنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَڢَطَا وَدُكَنْ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ وَطَنْدَ سُكٜىٰ ذَمَ عَڧَسَرْ مَصَرْ؞ نَا ضَنْڟٜىٰ دَ سُونَنَ مَيْغِرْمَ، بَا كُواْ طَيَ دَغَ ثِكِنْ يَهُودَاوَا أَ مَصَرْ دَ ذَيْسَاكٜىٰ عَمْبَتَرْ سُونَنَ؞ بَاوَنْدَ ذَيْ ڢَطَا، ‹نَا ضَنْڟٜىٰ دَ سُونَنْ عُبَنْغِجِ يَهْوٜىٰهْ مَيْ رَيْ؞› نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuza da yake zaune a ƙasar Masar. ‘Ni Ubangiji na rantse da sunana Maɗaukaki, cewa ba zan yarda kuma wani mutumin Yahuza da yake ƙasar Masar ya ambaci sunana da yin rantsuwa, cewa ya rantse da zatin Ubangiji ba.’